Idan mutum yana cikin yin sahur, sai ya ji kiran sallah yaya zai yi?( Sheikh Abdulwahhab Abdullah)


AMSA:
A irin wannan hali mutum zai
qarasa abin da ke hannunsa ne.
Domin hadisi ya tabbata daga Abu
Huraira radhiyallahu anhu ya ce:
Manzon Allah sallallahu alaihi wa
sallama ya ce:
ﺇِﺫَﺍ ﺳَﻤِﻊَ ﺃَﺣَﺪُﻛُﻢْ ﺍﻟﻨِّﺪَﺍﺀَ ﻭَﺍﻟْﺈِﻧَﺎﺀُ ﻋَﻠَﻰ ﻳَﺪِﻩِ ﻓَﻠَﺎ
ﻳَﻀَﻌْﻪُ ﺣَﺘَّﻰ ﻳَﻘْﻀِﻲَ ﺣَﺎﺟَﺘَﻪُ ﻣِﻨْﻪُ
Ma’ana:
Idan dayanku ya ji kiran sallah
alhali qwarya tana hannunsa, kada
ya ajiye ta, har sai ya biya
buqatarsa .
Amma a nan sai a yi hattara, kada
a mayar da irin wannan dabi`a ta
zama al`ada a kullum domin ba
ance mustahabbi bane yin hakan
ballantana a ce ana so a rinqa yi,
sassauci ne akayi ga wanda ya
fara cin abinci sai lokaci ya kure
masa.
wa sallallahu wa sallama ala
Nabiyyina Muhammadin wa ala
aa’lihi wa sahbihi ajma’in.